Isa ga babban shafi

An fara tattaunawar neman zaman lafiyar Chadi a Qatar

Gwamnatin mulkin sojan kasar Chadi da kungiyoyin 'yan adawa da dama sun fara tattaunawar zaman lafiya a Qatar domin kawo karshen matsalar tawaye a kasar da kuma gudanar da zabe.

Fira Ministan Chadi Albert Pahimi Padacke a farkon tattaunawar zaman lafiyar Chadi a Doha babban birnin Qatar, ranar 13 ga Maris, 2022.
Fira Ministan Chadi Albert Pahimi Padacke a farkon tattaunawar zaman lafiyar Chadi a Doha babban birnin Qatar, ranar 13 ga Maris, 2022. © KARIM JAAFAR / AFP
Talla

Firaministan kasar Chadi Albert Pahimi Padacke da shugaban hukumar Tarayyar Afirka Moussa Faki Mahamat sun shaidawa mahalarta taron cewa a ranar Lahadi cewa, dole ne bangarorin biyu su hakura da wasu daga cikin kudurorinsu domin cimma kyakkyawar matsaya.

Kungiyoyin ‘yan tawaye da na 'yan adawa 44 ne aka gayyata zuwa taron tattaunawar sulhun na Chadi da ke gudana a birnin Doha na kasar Qatar, wanda ya kamata a ce a fara gudanar da shi, daga ranar 27 ga watan Fabrairu.

Chadi ta fada cikin rudani a watannin baya bayan nan, biyo bayan kashe tsohon shugaban kasar Idriss Deby Itno yayin fafatawa da 'yan tawaye a arewacin kasar cikin watan Afrilun da ya gabata, abinda ya sanya dansa Mahamat Idriss Deby Itno, ya karbi ragamar mulkin kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.